Zai Yiwu A Sake Rayuwa

Transcript

Zai Yiwu A Sake Rayuwa
SATUM BA – O KTO BA 2 0 1 5
34567
Zai Yiwu A Sake Rayuwa
BAYAN MUTUWA?
34567
Vol. 136, Na 17
˙
Bugun Kowace Fitowa:
52,946,000 A HARSUNA 243
SATUMBA–OKTOBA 2015
Monthly and supplemental
bimonthly editions
HAUSA
WANNAN MUJALLAR, Hasumiyar
Tsaro, ana buga ta ne don girmama
Jehobah Allah, Mamallakin sama da
asa. Tana arfafa mutane cewa
Mulkin Allah zai kawar da dukan
mugunta kuma ya mai da duniya
aljanna ba da daewa ba. Tana sa a
ba da gaskiya ga Yesu Kristi, wanda
ya mutu domin mu sami rai
madawwami kuma wanda a yanzu shi
ne Sarkin Mulkin Allah. An soma
buga wannan mujallar babu fashi tun
daga shekara ta 1879. Wannan
mujallar ba ta siyasa ba ce. Littafi
Mai Tsarki ne madogaranta.
ABIN DA KE SHAFIN FARKO
Za ka so arin bayani ko
kuwa nazarin Littafi Mai
Tsarki a gidanka kyauta?
A FITOWAR NAN
Zai Yiwu A Sake Rayuwa—Bayan
Mutuwa? SHAFUFFUKA NA 3-8
Mene ne Ke Faruwa da Mu Bayan Mutuwa? 3
Matattu Suna da Bege Kuwa? 5
Me Zai Iya Tabbatar Maka Cewa Matattu Za Su
Sake Rayuwa? 7
Ka Sani? 9
Littafi Mai Tsarki Yana Gyara Rayuwar Mutane
Ka shiga dandalin
www.jw.org/ha ko kuma
ka aika sao zuwa ga aya
daga cikin waannan
adireshin da ke asa.
Na NIJERIYA:
Jehovah’s Witnesses
P.M.B. 1090
Benin City 300001
Edo State
¯
Na Yi Rayuwar Banza Sosai a Da 10
Za Mu Iya Faranta wa Allah Rai Kuwa? 12
Ka Sani? 15
Amsoshin Tambayoyi Daga Littafi Mai Tsarki 16
Na BENIN:
´
´
Les Temoins de Jehovah
B.P. 312
AB-Calavi
Za ka sami cikakken jerin adireshinmu a
www.jw.org/ha/hanyar-tuntuba.
˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙˙
Wannan mujallar ba ta sayarwa ba ce. Sashe ce
ta aikin ilimantarwa na Littafi Mai Tsarki a dukan
duniya wadda ake tallafa wa da gudummawar da
aka ba da da son rai. An auko nassosin da aka
yi amfani da su a nan ne daga Littafi Mai Tsarki
Cikin Tsohuwar Hausa a Sauae. A duk inda
kuka ga an rubuta LMT, ana nufin an yi aulin
wata fassarar Littafi Mai Tsarki ne. Idan kuma
kuka ga NW, ana nufin an yi aulin fassarar New
World Translation.
The Watchtower (ISSN 0043-1087) is published
semimonthly by Watchtower Bible and Tract
Society of New York, Inc.; L. Weaver, Jr.,
President; G. F. Simonis, Secretary-Treasurer;
25 Columbia Heights, Brooklyn, NY 11201-2483,
and by Watch Tower Bible and Tract Society of
Canada, PO Box 4100, Georgetown, ON L7G 4Y4.
Periodicals Postage Paid at Brooklyn, NY, and at
additional mailing offices. POSTMASTER: Send
address changes to Watchtower, 1000 Red Mills
Road, Wallkill, NY 12589-3299. 5 2015 Watch
Tower Bible and Tract Society of Pennsylvania.
Printed in Nigeria.
s
ZA KA SAMI ARIN BAYANI A INTANE
AMSOSHI GA ARIN TAMBAYOYI
DAGA LITTAFI MAI TSARKI
SATUM BA – O KTO BA 2 0 1 5
34567
Me Zai Taimaka Mini In
Daina Tsoron Mutuwa?
Zai Yiwu A Sake Rayuwa
BAYAN MUTUWA?
KA SAUKO DA
WANNAN
MUJALLAR
A DANDALINMU
r
5 sablin/123RF Stock Photo
(Ka danna KOYARWAR LITTAFI MAI
TSARKI ˛ AN AMSA TAMBAYOYIN
LITTAFI MAI TSARKI)
ABIN DA KE SHAFIN FARKO
Mene ne Ke Faruwa
da Mu Bayan
Mutuwa?
“Na auka cewa idan mutum ya mutu yana
iya zuwa wurare uku, wato sama ko gidan
wuta ko kuma purgatori. Na san cewa ban
cancanci zuwa sama ba kuma ban yi
abubuwan da suka isa in shiga gidan wuta
ba. Ban san ainihi abin da purgatori yake
nufi ba. Ban taa ganin kalmar a cikin Littafi
Mai Tsarki ba, age ne kawai.”—In ji Lionel.
“An koya mini cewa dukan waanda suka
mutu suna zuwa sama amma ban gamsu da
hakan ba. Na ga kamar mutuwa ce arshen
kome, wato babu wani bege ga matattu.”
—In ji Fernando.
Ka taa yin irin wannan tambayar: ‘Mene ne
ke faruwa da mutane sa’ad da suka mutu?
Matattu suna shan azaba a wani wuri ne?
Za mu sake ganinsu kuwa? Ta yaya za mu
tabbata da hakan?’ Don Allah ka yi la’akari
da abin da Littafi Mai Tsarki ya faa game da
wannan batun. Bari mu fara bincika yadda
Littafi Mai Tsarki ya kwatanta mutuwa.
Bayan haka, sai mu tattauna begen da Littafi
Mai Tsarki ya yi magana a kai.
SATUMBA–OKTOBA 2015
3
Mene ne yanayin matattu?
ABIN DA LITTAFI MAI TSARKI YA CE: “Masu-rai sun san za
TASHIN MATATTU TAKWAS DA AKA
AMBATA A LITTAFI MAI TSARKI1
Yaron wata gwauruwa Annabi Iliya ya ta da
yaron wata gwauruwa da ke Zarefat a arewacin
Isra’ila.—1 Sarakuna 17:17-24.
an wata Ba-shunammiya Elisha magajin annabi Iliya ya ta da wani yaro a garin Shunem
kuma ya mia shi ga iyayensa.—2 Sarakuna 4:
32-37.
Wani mutum a makabarta An binne gawan
wani da bai dae da mutuwa ba a inda aka
binne annabi Elisha. Mutumin ya tashi sa’ad da
gawarsa ta taa asusuwan annabi Elisha.
—2 Sarakuna 13:20, 21.
an wata gwauruwa a auyen Nayin Yesu
ya dakatar da wata jana’izar da ake yi a garin
Nayin kuma ya ta da wannan matashin, ya mai
da shi ga mahaifiyarsa da ke makoki.—Luka 7:
11-15.
’Yar Yariyus Wani ma’aikacin majami’a mai
suna Yariyus ya kira Yesu don ya warkar da
’yarsa da ke rashin lafiya. Yesu ya ta da ita jim
kaan bayan ta rasu.—Luka 8:41, 42, 49-56.
Li’azaru, abokin Yesu Yesu ya ta da Li’azaru
bayan kwanaki huu da mutuwa kuma mutane
da yawa sun shaida wannan aukuwar.—Yohanna 11:38-44.
Wata mai suna Dokas Manzo Bitrus ya ta da
wannan matar wadda aka san ta da ayyukan
nagarta.—Ayyukan Manzanni 9:36-42.
Aftikos Manzo Bulus ya ta da wani matashi
mai suna Aftikos da ya fao daga tagar wata
bene.—Ayyukan Manzanni 20:7-12.
1 Tashin matattu mafi muhimmanci shi ne na Yesu Kristi
kuma ya bambanta da waannan takwas da muka tattauna. Abin da za a tattauna a talifi na gaba ke nan.
4
HASUMIYAR TSARO
su mutu: amma matattu ba su san kome ba, ba su kuwa
da sauran lada; gama ba a ara tuna da su ba. Dukan abin
da hannunka ya iske na yi, ka yi shi da arfinka; gama
babu wani aiki, ko dabara, ko ilimi, ko hikima, cikin kabari inda za ka.”1—Mai-Wa’azi 9:5, 10.
Kabari wuri ne da ake saka mutane sa’ad da suka
mutu, ba wuri ne na zahiri ba domin mutanen da
suke wurin ba su san kome ba kuma ba sa aiki. Wane
ra’ayi ne Ayuba mai aminci yake da shi game da Kabari? Ya yi asarar dukiyarsa da ’ya’yansa a rana aya
kuma Shaian ya addabe shi da gyambuna. Ya roi
Allah: “Da fa za ka yarda ka oye ni cikin Lahira [‘Kabari,’ New World Translation].” (Ayuba 1:13-19; 2:7;
14:13) Hakika, Ayuba bai auka cewa Kabari gidan
wuta ba ne inda wahalar da yake sha za ta daa aruwa ba. Maimakon haka, ya san cewa wurin hutu ne.
Akwai wata hanya kuma da za mu iya koya game da
yanayin matattu. Littafi Mai Tsarki yana auke da labaran mutane takwas da suka tashi daga mutuwa da
za mu iya yin bincike a kansu.—Ka duba akwatin nan
“Tashin Matattu Takwas da Aka Ambata a Littafi Mai
Tsarki.”
Babu ko aya cikin mutane takwas da aka ambata
da ya je sama ko kuma gidan wuta. Da a ce waanda
aka tashe su sun je irin waannan wuraren, kana ganin da ba su ba mutane labari ba? Kuma da ba a rubuta hakan a cikin Littafi Mai Tsarki don mutane su
karanta ba? Ba a rubuta kome game da hakan a cikin
Littafi Mai Tsarki ba. Babu shakka, waannan mutane takwas ba su ce kome ba game da wannan batun.
Me ya sa? Domin a lokacin da suka mutu ba su san
kome ba, kamar sun yi barci ne mai zurfi. Hakika a
wasu lokuta, Littafi Mai Tsarki yakan kwatanta mutuwa da barci. Alal misali, amintattun mutane kamar
Dauda da Istafanus sun “yi barci,” wato sun mutu.
—Ayyukan Manzanni 7:60; 13:36.
To, wane bege ne matattu suke da shi? Za su iya
farka daga wannan barci kuwa?
1 An yi amfani da kalmar nan “Kabari” a wuraren da kalmomin Ibranancin nan “Sheol” da kuma na Helenanci “Hades” suka bayyana.
Wasu juyin Littafi Mai Tsarki sun yi amfani da kalmar nan “jahannama”
amma Littafi Mai Tsarki bai koyar da cewa ana one mutane a wuta ba.
Matattu Suna da Bege Kuwa?
Shin matattu za su sake
rayuwa kuwa?
ABIN DA LITTAFI MAI TSARKI YA CE: ‘Sa’a tana zuwa,
inda dukan waanda suna cikin kabarbaru za su ji muryar [Yesu], su fito kuma.’—Yohanna 5:28, 29.
Yesu ya yi annabci a kan lokacin da za a ta da dukan
mutanen da suke cikin Kabari sa’ad da ya soma sarauta. Fernando da aka ambata a talifi na farko ya
ce: “Na yi mamaki sosai a lokacin da na fara karanta littafin Yohanna 5:28, 29. Hakan ya sa na kasance
da bege sosai kuma na soma yin tunani game da nan
gaba da gaba gai.”
¯ Ayuba mai aminci ya sa rai cewa
A zamanin da,
Allah zai ta da shi idan ya mutu. Ayuba ya yi wannan
Tashin Li’azaru daga
mutuwa ya sa mun
kasance da bege
tambayar: “Idan mutum ya mutu za ya sake rayuwa?” Sai ya amsa da gaba gai: “Dukan kwanakin
yaina [lokacin da nake kabari] sai in jira, har a kare ni in huta. Za ka yi kira, ni ma in amsa maka.”
—Ayuba 14:14, 15.
Tashin matattu ba sabon abu ba ne ga Martha,
’yar’uwar Li’azaru. Bayan Li’azaru ya mutu, Yesu ya
ce mata: “an’uwanki zai tashi kuma.” Martha ta ce
masa: “Na sani za ya tashi kuma a cikin tashin matattu a kan rana ta arshe.” Sai Yesu ya ce mata: “Ni
ne tashin matattu, ni ne rai: wanda ya ba da gaskiya
gare ni, ko ya mutu, zai rayu.” (Yohanna 11:23-25)
Bayan haka, sai Yesu ya ta da Li’azaru daga mutuwa! Wannan labarin soma tai ne na abin da zai faru
a nan gaba. Ka yi tunanin yadda rayuwa za ta kasance idan an ta da matattu a dukan duniya!
Shin za a ta da wasu zuwa
sama ne?
ABIN DA LITTAFI MAI TSARKI YA CE: Kalmar Allah ta
nuna cewa tashin Yesu da aka yi daga mutuwa ya
bambanta da guda takwas da aka ambata a cikin
Littafi Mai Tsarki. An ta da waannan mutane takwas a duniya. Amma ga abin da nassi ya ce game da
na Yesu: “Yesu Kristi; shi wanda ke ga hannun dama na
Allah, ya rigaya ya hau sama.” (1 Bitrus 3:21, 22) Ban
da Yesu, shin da akwai wasu kuma da za a ta da zuwa
sama? Yesu ya ce wa manzanninsa: “In kuwa na je na
shirya muku wuri, sai in dawo in kai ku wurina, domin inda nake, ku ma ku zama kuna can.”—Yohanna
14:3, Littafi Mai Tsarki.
Kristi ya je sama kuma ya yi shirye-shirye don zuwan wasu cikin almajiransa. Adadin mutane 144,000 ne za su je sama. (Ru’ya ta Yohanna 14:1, 3)
Amma mene ne waannan mabiyan Yesu za su yi a
sama?
SATUMBA–OKTOBA 2015
5
Dukan mutanen da suke bauta wa Allah za su yi rayuwa har abada
cikin oshin lafiya da kuma farin ciki
Za su yi aiki tuuru! Littafi Mai Tsarki ya ce: “Maialbarka kuma mai-tsarki ne shi wanda yake da rabonsa cikin tashi na fari: mutuwa ta biyu ba ta da
iko bisansu; amma za su zama firistoci na Allah
da na Kristi, za su yi mulki kuma tare da shi shekara
dubu.” (Ru’ya ta Yohanna 20:6) Mutanen da za a ta
da zuwa sama za su zama sarakuna da kuma firistoci tare da Kristi kuma za su yi sarauta bisa duniya.
Su waye za a tayar daga baya?
ABIN DA LITTAFI MAI TSARKI YA CE: An rubuta wannan
furucin manzo Bulus cikin Nassosi: “Ina da bege ga
Allah, abin da waannan da kansu kuma suna sauraronsa, za a yi tashin matattu, na masu adalci da na marasa
adalci.”—Ayyukan Manzanni 24:15.
Su waye ne “masu adalci” da Bulus ya ambata? Ga
wani misali. Daniyel mutumi ne mai adalci kuma
sa’ad da ya kusan mutuwa, an gaya masa cewa: Za
“ka huta, a arshen kwanaki za ka tashi ka kari
naka rabo.” (Daniyel 12:13, LMT) A ina ne za a ta da
¯ aDaniyel daga mutuwa? “Masu-adalci za su gaji
san, su zauna a cikinta har abada.” (Zabura 37:29)
Kuma Yesu ya yi wannan annabcin: “Masu-albarka
¯ duniya.” (Matne masu-tawali’u: gama su za su gaji
ta 5:5) Za a ta da Daniyel da kuma wasu amintattun
maza da mata don su sake rayuwa a duniya har
abada.
Su waye ne “marasa adalci” da Bulus ya ambata?
Su biliyoyin mutane ne da suka mutu, da yawa cikinsu ba su sami zarafin fahimta da kuma aikata gaskiyar da ke cikin Littafi Mai Tsarki ba. Bayan sun tashi daga mutuwa, za su sami zarafin sanin Jehobah1
da kuma Yesu. (Yohanna 17:3) Dukan mutanen da
suka yanke shawarar bauta wa Allah za su yi tsawon rayuwa kamar Jehobah, wato za su rayu har
abada.
Yaya rayuwa za ta kasance a
duniya?
ABIN DA LITTAFI MAI TSARKI YA CE: Allah “zai share du-
Kalmar Allah ta tabbatar
mana cewa biliyoyin
mutanen da suka mutu
za su sake rayuwa
kan hawaye kuma daga idanunsu: mutuwa kuwa ba za ta
ara kasancewa ba; ba kuwa za a ara yin bain ciki, ko
kuka, ko azaba.” (Ru’ya ta Yohanna 21:4) “Za su gina
gidaje, kuma za su zauna a ciki; su yi gonakin anab
kuma, su ci amfaninsu.”—Ishaya 65:21.
Ka yi tunanin yadda rayuwa za ta kasance sa’ad da
kake cikin irin wannan yanayin tare da mutanen da
aka tayar daga mutuwa! Amma akwai wata tambaya
da ba a amsa ba tukun, Ta yaya za ka kasance da tabbaci cewa za a ta da matattu?
1 Littafi Mai Tsarki ya nuna cewa Jehobah shi ne sunan Allah.
6
HASUMIYAR TSARO
Me Zai Iya Tabbatar Maka Cewa
MATATTU ZA SU SAKE RAYUWA?
Shin ata lokaci ne yin tunani cewa matattu za su
sake rayuwa? Manzo Bulus bai kasance da wannan
ra’ayin ba. Allah ya hure shi ya ce: “Da begenmu ga
Almasihu domin wannan rai ne kaai, ai, da mun fi
kowa zama abin tausayi. Amma ga hakika an ta da
Almasihu daga matattu, shi ne ma nunan fari na
waanda suka yi barci.” (1 Korintiyawa 15:19, 20,
Littafi Mai Tsarki) Bulus yana da tabbaci sosai cewa
za a ta da matattu. Tashin Yesu daga mutuwa ne
ya ba da wannan tabbacin.1 (Ayyukan Manzanni
17:31) Shi ya sa Bulus ya kira Yesu “nunan fari,” domin shi ne mutumi na farko da ya tashi daga mutuwa da ba zai sake mutuwa ba har abada. Idan Yesu
ne na fari, to babu shakka, akwai wasu da za su
biyo bayansa.
Ga wani dalili kuma da ya sa za mu iya gaskatawa da begen tashin matattu. Jehobah Allah yana
fain gaskiya a koyaushe. “Allah . . . ba ya iya yin
arya.” (Titus 1:2) Jehobah bai taa yin arya ba
kuma ba zai taa yin hakan ba. Shin zai yiwu ya yi
mana alkawarin tashin matattu, ya nuna cewa yana
da ikon yin hakan, sa’an nan daga baya ya fasa cika
alkawarinsa? Babu shakka, hakan ba zai yiwu ba!
Me ya sa Jehobah ya yi alkawari cewa zai ta da
matattu? Domin yana aunarmu. Ayuba ya yi wannan tambayar: ‘Idan mutum ya mutu za ya sake rayuwa? . . . Za ka yi kira, ni ma in amsa maka: Za ka
yi marmarin aikin hannuwanka.’ (Ayuba 14:14, 15)
Ayuba ya tabbata cewa Ubansa na sama zai yi marmarin tayar da shi. Shin Allah ya canja ne? Jehobah
¯
ya ce: “Ni Ubangiji ba mai-sakewa
ba ne.” (Malakai
3:6) Har ila, Allah yana okin tayar da waanda
suka mutu kuma su kasance da oshin lafiya da farin ciki. Abin da mahaifi mai auna zai so ya faru
Ayuba ya gaya wa Allah: “Za ka yi marmarin aikin
hannuwanka.”—Ayuba 14:14, 15
1 Don tabbaci cewa an ta da Yesu daga mutuwa, ka duba Hasumiyar
Tsaro ta 15 ga Nuwamba, 2014, shafi na 6, sakin layi na 11-14.
SATUMBA–OKTOBA 2015
7
Mutuwa maiyiya ce, amma
Allah zai kawar da ita
ke nan bayan ansa da ya mutu. Bambancin shi ne
Allah yana da ikon yin abin da ya nufa.—Zabura
135:6.
Jehobah zai ba ansa iko ya sa masu makoki su
yi matuar farin ciki. Mene ne ra’ayin Yesu game da
tashin matattu? Yesu ya yi “kuka” kafin ya tayar
da Li’azaru don ya ga irin bain ciki da ’yan’uwansa
da kuma abokansa suka yi. (Yohanna 11:35) A wani
lokaci kuma, Yesu ya ga wata gwauruwa a auyen
Nayin da anta tilo ya mutu. Yesu “ya ji tausayinta,
ya kuma ce mata, ‘Daina kuka.’ ” Nan da nan sai ya
tayar da anta. (Luka 7:13, LMT) Saboda haka, Yesu
ba ya jin dain ganin mutane suna makoki da kuma
mutuwa. Zai yi murna sosai sa’ad da ya sa dukan
mutanen da ke makoki a duniya baki aya farin ciki!
An taa maka rasuwa kuwa? Za ka iya auka cewa
ba za a iya kawar da mutuwa ba. Amma hakan ba
gaskiya ba ne, Allah zai yi amfani da ansa don ya
tayar da mutanen da suka rasu. Ka tuna cewa Allah
yana so ka shaida lokacin da za a ta da matattu. Yana
so ka kasance a wurin don ka marabci ’yan’uwanka
da za a tayar daga mutuwa. Ka yi tunanin yadda rayuwa za ta kasance sa’ad da mutuwa ta zama tsohon
labari!
Lionel da aka ambata azun ya ce: “Daga baya sai
na koya cewa za a yi tashin matattu. Da farko, ban
gaskata da hakan ba domin na yi shakkar mutumin
da ya gaya mini. Amma da na bincika Littafi Mai
Tsarki sai na ga cewa hakan gaskiya ne! Ina okin
sake ganin kakana.”
Za ka so ka sami arin bayani? Shaidun Jehobah
za su yi farin cikin nuna maka a cikin naka Littafi
Mai Tsarki cewa za a ta da matattu.1 ˇ
1 Ka duba babi na 7 na littafin nan Menene Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake
Koyarwa? da Shaidun Jehobah suka wallafa. Za ka kuma iya samunsa
a dandalin www.jw.org/ha.
8
HASUMIYAR TSARO
KA SANI?
Kamar yadda yake a cikin Littafi Mai Tsarki,
¯
mene ne kalmar nan baba take nufi?
¯
HOTON BABA A ASIRIYA
5 The Metropolitan Museum of Art,
Image source: Art Resource, NY
¯
A wasu lokuta, ana amfani da kalmar nan baba don a kwatan¯
ta namijin da aka yi masa dandae. A da, an yi wa wasu maza
dandae don sun yi wani laifi ko bayan an ci su a yai ko kuma
sa’ad da suka zama bayi. Ana amfani da mazan da aka yi musu
dandae wajen gadin matan sarki ko kuma wani attajiri. Alal mi¯
sali, baba Hegai da Sha’ashgaz sun yi aiki ne a matsayin masu
gadin matan Sarki Ahasurus ko kuma Xerxes na aya.—Esther
2:3, 14.
¯
Amma ba dukan waanda Littafi Mai Tsarki ya kira su baba
ne aka yi musu dandae ba. Wasu masana sun ce kalmar
tana da manufa da yawa, tana iya nufin wani babban ma’aikaci a fadar sarki. Wataila abin da ya sa Littafi Mai Tsarki ya ce da
¯
Ebed-melech, abokin aikin Irmiya baba kuma ya ce da wani Bahabashe wanda Filibus ya yi ma wa’azi ma hakan. Ebed-melech
babban ma’aikacin sarki ne don yana da ’yancin zuwa wurin
Sarki Zedekiya. (Irmiya 38:7, 8) Kuma an kwatanta Bahabashen a matsayin ma’ajin sarauniya da ya je “Urushalima . . . garin yin sujada.”—Ayyukan Manzanni 8:27. ˇ
¯
Me ya sa makiyaya a zamanin da suke ware
tumaki daga awaki?
5 World Religions Photo Library/Alamy
Sa’ad da Yesu yake kwatanta hukuncin da za a yi a nan
gaba, ya ce: ‘Sa’ad da an Mutum ya zo cikin aukaka
tasa . . . zai kuma ware mutane dabam-dabam, kamar yadda makiyayi ke ware tumaki da awaki.’ (Matta 25:31, 32, Littafi Mai Tsarki) Me ya sa makiyaya suke ware tumaki daga
awaki?
Ana yawan yin kiwon awaki da tumaki tare da rana. Amma
daddare, ana shinge su saboda namomin daji ko arayi ko
kuma sanyi. (Farawa 30:32, 33; 31:38-40) Ana ware tumaki
daga awaki domin kada awakin su ji wa tunkiya ko kuma ’ya’yansu rauni. Littafin nan All Things in the Bible ya ce: “Makiyaya suna kuma ware tumaki daga awaki sa’ad da suke tatse nono da yanke gashinsu da kuma sa’ad da suka haihu.”
Saboda haka, kwatancin Yesu sananne ne ga masu sauraronsa da ke zama a wuraren da ake kiwo kamar a asar Is¯
ra’la ta da. ˇ
SATUMBA–OKTOBA 2015
9
LITTAFI MAI TSARKI YANA GYARA RAYUWAR MUTANE
Na yi rayuwar banza
¯
sosai a da
STEPHEN MCDOWELL
NE YA BA DA LABARIN
SHEKARAR HAIHUWA
1952
ASAR HAIHUWA
AMIRKA
TARIHI
MAI ZAFIN RAI
¯
RAYUWATA A DA: Na yi girma a birnin Los Angeles, Kalifoniya a asar
Amirka kuma na zauna a unguwar da ke cike da ’yan iska da kuma
masu shan miyagun wayoyi. Iyayena sun haifi yara shida kuma ni ne
na biyu a cikinsu.
Mahaifiyarmu ta rene mu a wani coci mai suna evangelical church.
Amma sa’ad da nake tsakanin shekara sha uku zuwa sha tara, na soma
yin rayuwar banza. A ranar Lahadi nakan yi waa a cocinmu. A wasu
ranakun kuma sai in je fati, in sha miyagun wayoyi kuma in yi lalata.
Ina yawan fushi da kuma zafin rai. Ina amfani da kowane abu don
in ji ma mutane rauni. Abin da na koya a coci bai taimaka mini ba sam.
Nakan ce, “Ramako na Ubangiji ne, kuma da ni zai cim ma hakan!”
Sa’ad da nake makarantar sakandare a arshen shekara ta 1960, na
shiga wani rukunin da ke yai don ’yancin alibai. Wani rukunin siyasa da ke yai don ’yancin masu farar hula da ake kira Black Panthers ne
ya rinjaye ni yin hakan. A lokatai da yawa mukan ta da rigima har ma
a rufe makarantar na an lokaci.
Ban gamsu da zanga-zanga da nake yi ba, saboda haka, na soma aikata laifi don ina iyayyar mutane. Alal misali, akwai lokacin da muka
kalli wani fim da ya nuna yadda ’yan Amirka suke wulaanta ’yan Afir¯ Da muka ji haushi, sai muka yi wa turawan da ke gidan siliman
ka a da.
¯
dukan
tsiya. Bayan haka, sai muka shiga unguwoyi muna neman tura¯
wan za mu yi wa duka.
Da na kusan shekara ashirin, ni da annena biyu da kuma yayana
mun ware sosai a aikata manyan laifuffuka. Saboda haka, muna yawan
samun saani da hukuma. anina yana cikin wani sanannen rukuni mai
ta da rikici, kuma ni ma ina bin su. Rayuwata sai daa muni take yi.
YADDA LITTAFI MAI TSARKI YA CANJA RAYUWATA: Ina da abokin da
iyayensa Shaidun Jehobah ne. Sun gayyace ni zuwa taronsu kuma na
je. Wannan ne aro na farko da na ga cewa halin Shaidun Jehobah
dabam ne. Na lura cewa kowa yana amfani da Littafi Mai Tsarki
a taron kuma matasa ma suna yin jawabai! Na yi farin cikin sanin
cewa sunan Allah Jehobah ne kuma na ji suna amfani da shi. (Zabura
83:18) Babu wata wariya a ikilisiyar duk da cewa mutanen daga kabilu
dabam-dabam ne.
Da farko na so halartan taron Shaidun Jehobah amma ban so yin
nazarin Littafi Mai Tsarki da su ba. Akwai wata rana da na je taron
10
HASUMIYAR TSARO
Shaidun Jehobah da yamma, amma abokaina kuma
sun je fati. A wurin suka kashe wani matashi don ya
i ya ba su kwat insa. Washegari, sai suka yi ta cika
baki game da kisan da suka yi. Sa’ad da aka kai su
kotu, ba su auka cewa sun aikata babban laifi ba. A
sakamakon haka, an yi wa yawancinsu aurin rai da
rai. Na yi farin ciki cewa ban bi su a wannan ranar
ba. A lokacin ne na tsai da shawarar canja rayuwata
da kuma soma nazarin Littafi Mai Tsarki.
Da yake na saba gani ana nuna wariyar kabila, hakan ya sa ni mamaki sosai sa’ad da na lura cewa halin Shaidun Jehobah dabam ne. Alal misali, akwai
lokacin da wani bature ya tafi asarsu kuma ya bar
yaransa a hannun wani bain fata don ya kula da su.
Ban da wannan ma, na ga wani iyalin turawa sun ce
wa wani matashi bain fata da ke neman gida ya zo
ya zauna da su. Hakan ya sa na gaskata cewa Shaidun Jehobah ne suka yi daidai da kwatancin Yesu a
Na yi oari sosai in canja salon
rayuwata don in yi zaman lafiya da
mutane kuma na tabbata cewa
wannan ita ce hanyar da ta dace
littafin Yohanna 13:35 cewa: “Bisa ga wannan mutane duka za su fahimta ku ne almajiraina, idan kuna
da auna ga junanku.” Wannan ya sa na yarda cewa
na sami addini na gaskiya.
Nazarin Littafi Mai Tsarki da nake yi ya sa na fahimta cewa ya kamata in canja ra’ayina. Na yi oari
sosai in canja salon rayuwata don in yi zaman lafiya
da mutane kuma na tabbata cewa wannan ita ce hanyar da ta dace. (Romawa 12:2) Da sannu-sannu na
samu ci gaba kuma a watan Janairu na shekara ta
1974, na yi baftisma a matsayin Mashaidin Jehobah.
Amma har bayan na yi baftisma, na ci gaba da yin
oari don in rage zafin rai. Alal misali, na taa bin
wani arawo da ya saci rediyo a motata sa’ad da
nake wa’azi. Da ya ga cewa na yi kusa da shi, sai ya
yar da rediyon ya gudu. Sa’ad da na gaya wa waan-
da muke wa’azi tare da su abin da ya faru, sai wani
dattijo a cikinsu ya tambaye ni, “Stephen, da a ce ka
kama shi me za ka yi masa?” Tambayar ta sa in san
cewa ina bukatar in yi oari don in zauna lafiya da
mutane.
A watan Oktoba ta 1974, na soma hidima ta cikakken lokaci, ina yin sa’o’i ari a kowane wata don
koya wa mutane Littafi Mai Tsarki. Daga baya, an
gayyace ni yin hidima a hedkwatar Shaidun Jehobah da ke Brooklyn, a Amirka. A shekara ta 1978, na
koma birnin Los Angeles don in kula da mahaifiyata da ke rashin lafiya. Bayan shekara biyu, sai na auri
wata mai suna Aarhonda. Ta taimaka mini sosai wajen kula da mahaifiyata har zuwa lokacin da ta rasu.
Bayan haka, sai aka gayyace mu zuwa Makarantar
Littafi Mai Tsarki ta Gilead kuma da muka sauke karatu, an tura mu zuwa asar Panama, inda muka yi
hidima a matsayin masu wa’azi a asashen waje.
Tun da na yi baftisma, na fuskanci wasu yanayoyin da za su iya sa in yi faa. Amma na yi oarin
guje wa mutanen da suke so su sa ni fushi ko kuma
ina yin amfani da wata dabara don kada abin ya jawo
faa. Matata da mutane da yawa sun yaba mini don
yadda na bi da waannan yanayoyin kuma yadda na
bi da yanayin ya ba ni mamaki sosai. Na san cewa ba
da ikona nake yin waannan canje-canjen ba. Maimakon haka, na tabbata cewa Littafi Mai Tsarki ne
ya taimaka mini in yi hakan.—Ibraniyawa 4:12.
YADDA NA AMFANA: Littafi Mai Tsarki ya taimaka
mini in yi rayuwa mai ma’ana kuma in zauna lafiya
¯
da mutane. Na daina dukan
mutane yanzu, amma
ina taimaka musu su san Allah. Har ma na yi nazarin
Littafi Mai Tsarki da wani da muke yawan faa da shi
sa’ad da muke makaranta. Bayan da ya yi baftisma,
mun soma zama a dai aya da shi. Har wa yau, mu
abokai ne sosai. Tun daga lokacin har zuwa yau, mun
yi nazarin Littafi Mai Tsarki da mutane sama da 80
kuma sun zama Shaidun Jehobah.
Ina godiya ga Jehobah sosai don ya taimaka mini
in yi rayuwa mai ma’ana da farin ciki a tsakanin ’yan’uwana Shaidun Jehobah. ˇ
SATUMBA–OKTOBA 2015
11
‘[Allah] ya ceci Lutu adali,
wanda fajircin kangararru
ya bakinta masa rai
warai.’—2 Bitrus 2:7
Za Mu Iya
Faranta wa
Allah Rai Kuwa?
Ka taa karanta labarin wasu da
aka yaba musu sosai a Littafi Mai
Tsarki kuma ka ce wa kanka, ‘Ba
zan iya zama kamar waannan
mutanen ba!’ Kana iya cewa, ‘Ni
ba kamili da kuma mai adalci ba
ne kuma ba na yin abin da ya
dace a koyaushe.’
12
HASUMIYAR TSARO
Littafi Mai Tsarki ya ce Ayuba “kamili ne maiadalci” kuma. (Ayuba 1:1) Ya kuma ce Lutu “maiadalci” ne. (2 Bitrus 2:8) Kuma ya ce Dauda ya “yi
abin da ke daidai” a idanun Allah. (1 Sarakuna
14:8) Amma bari mu tattauna wasu abubuwa game
da rayuwar waannan mutanen. Za mu ga cewa
sun yi (1) kura-kurai, (2) za mu iya koyan darussa
daga wurinsu, kuma (3) zai yiwu ’yan Adam ajizai
su faranta wa Allah rai.
SUN YI KURA-KURAI
Ayuba ya fuskanci matsaloli dabam-dabam
kuma ya ji kamar ana masa rashin adalci. Saboda
haka, ya kasance da ra’ayi marar kyau domin ya yi
zato cewa Allah bai damu ko shi mai adalci ne ko
marar adalci ba. (Ayuba 9:20-22) Ayuba ya tabbata sosai cewa shi mai adalci ne har ya soma ji kamar ya fi Allah adalci.—Ayuba 32:1, 2; 35:1, 2.
Lutu ya yi jinkirin yanke shawarar da ta dace.
Lalatar mutanen Saduma da Gwamarata ta sa shi
Dauda ‘ya bi [Allah] da
dukan zuciyarsa, domin
ya yi abin da ke daidai a
idanun [Allah] kaai.’
—1 Sarakuna 14:8
Ayuba “kamili ne
mai-adalci” kuma.
—Ayuba 1:1
bain ciki sosai har “ya azabtar da ransa maiadalci” domin ayyukansu. (2 Bitrus 2:8) Allah ya
gaya wa Lutu cewa yana so ya halaka biranen kuma
ya ba shi da iyalinsa damar tsere wa halakar. Shin
Lutu ya bar birnin da gaggawa kuwa? A’a. Ya yi jinkiri a wannan lokacin. Har sai da mala’ikan da aka
tura wajensu ya kama hannunsu kuma ya fitar da
su daga birnin.—Farawa 19:15, 16.
Dauda ya taa kasancewa da rashin kamun kai
kuma hakan ya sa ya yi zina da matar wani. Abin
bain ciki, ya kashe mijin matar garin neman ya
rufe wa kansa asiri. (2 Sama’ila, sura ta 11) Littafi
Mai Tsarki ya ce Jehobah “bai ji dain mugun abin
da Dauda ya yi ba.”—2 Sama’ila 11:27.
Ayuba da Lutu da kuma Dauda sun yi kurakurai, wasu masu tsanani ne sosai. Amma za mu
tattauna yadda suka nuna cewa suna so su bauta
wa Allah da aminci da kuma zuciya aya. Sun kasance a shirye su nuna cewa laifin da suka yi bai
dace ba kuma su yi gyara a inda suke bukatar yin
Allah “ya san abin da aka yi mu
da shi, yakan tuna, da ura
aka yi mu.”—Zabura 103:14
hakan. Shi ya sa Allah ya amince da su kuma Littafi Mai Tsarki ya ce su amintattu ne.
WANE DARASI NE ZA MU IYA KOYA?
Babu yadda za mu guji yin kura-kurai domin
mu ajizai ne. (Romawa 3:23) Amma idan hakan
ya faru, muna bukatar mu nuna cewa muna dana-sani kuma muna so mu yi gyara.
Ta yaya Ayuba da Lutu da kuma Dauda suka yi
gyara? Ayuba mutumi ne mai aminci. Sa’ad da Allah ya yi wa Ayuba gyara, ya amince da hakan
SATUMBA–OKTOBA 2015
13
Zuciya aya tana nufin zuciyar da ke aunar
Allah kuma ke son yin nufinsa
kuma ya yi da-na-sani don abubuwan da ya faa.
(Ayuba 42:6) Allah ya tsani lalatar da mutanen
Saduma da Gwamarata suke yi, Lutu ma haka. Matsalarsa kawai ita ce jinkirin da ya yi. Daga baya ya
fita daga birnin kuma ba a halaka shi ba. Lutu ya yi
biyayya ta wajen in juya baya don ya kalli abubuwan da ya bari. Ko da yake Dauda ya yi laifi mai tsanani ta wajen taka dokar Allah, ya tuba kuma ya
nemi gafara. Hakan ya nuna cewa yana aunar
Allah sosai.—Zabura ta 51.
Yadda Allah ya bi da waannan mutanen ya yi
daidai da ra’ayinsa game da ’yan Adam ajizai. Allah “ya san abin da aka yi mu da shi, yakan tuna,
da ura aka yi mu.” (Zabura 103:14, Littafi Mai
Tsarki) Idan Allah ya san cewa ba zai yiwu mu guji
yin kura-kurai ba, to, wane ra’ayi ne yake so mu kasance da shi?
TA YAYA MUTANE AJIZAI ZA SU IYA
FARANTA WA ALLAH RAI?
Shawarar da Dauda ya ba ansa Sulemanu ta
nuna abin da ya kamata mu yi don mu faranta wa
Allah rai. Dauda ya ce: “Kai kuwa ana Sulemanu,
sai ka san Allah na [ubanka], ka bauta masa da zuciya aya.” (1 Labarbaru 28:9, LMT) Mene ne furucin nan zuciya aya yake nufi? Yana nufin zuciyar
da ke aunar Allah kuma ke son yin nufinsa. Ba ya
nufin kamiltacciyar zuciya, amma zuciyar da ke
marmarin bauta wa Allah cikin aminci kuma take a
shirye ta yi gyare-gyare. Allah ya kira Ayuba “kamili,” Lutu “mai-adalci” kuma Dauda mutumin da
ke yin “abin da ke daidai” a idanun Allah a koyaushe domin sun aunace shi kuma sun yi okin yin
biyayya gare shi. Ko da yake sun yi kura-kurai,
amma sun yi abubuwan da suka faranta wa Allah
rai.
Saboda haka, idan mun yi tunanin banza ko
mun yi wani abu da daga baya muka san cewa
bai dace ba, ya kamata mu yi la’akari da misalan
da muka tattauna a wannan talifin. Allah ya san
cewa mu ajizai ne. Amma yana so mu aunace shi
kuma mu oarta don mu yi masa biyayya. Idan
muna bauta wa Allah da zuciya aya, za mu iya kasance da gaba gai cewa mu ma za mu iya faranta
masa rai. ˇ
14
HASUMIYAR TSARO
KA SANI?
Wane ’yanci ne manzo Bulus ya samu domin
ya zama an asar Roma?
BULUS YA CE: “A AUKAKA
ARATA GABAN KAISAR!”
Zama an asar Roma yana ba mutum ’yanci da kuma zarafi da
yawa a kowane wuri da ya shiga a cikin daular. Duk mutumin da ke
da ’yancin zama an asar Roma yana arashin dokar asar ne
ba na biranen da ke asar ba. Sa’ad da aka tuhume shi da aikata
laifi, za a iya shari’anta shi a birnin, amma yana da ’yancin aukaka ara zuwa babban kotun asar. Idan kuma an yanke masa hukuncin kisa, zai iya aukaka arar zuwa wajen sarkin asar.
Irin wannan ’yancin ne ya sa wani an siyasa a arni na farko kafin haihuwar Yesu, mai suna Cicero ya ce: “Kama an asar Roma
laifi ne; yi masa duka mugunta ne; kashe shi kuma aya ne da wani
ya kashe mahaifinsa ko mahaifiyarsa ko kuma wani danginsa.”
Manzo Bulus ya yi wa’azi sosai a Daular Roma. Ya yi amfani da
’yancinsa na an asar Roma a hanyoyi uku: (1) Ya gaya wa alalan Filibi cewa sun taka ’yancinsa ta wajen yi masa dua. (2) Sa’ad
da yake Urushalima, ya fai cewa shi an asar Roma ne domin
kada a doke shi. (3) Ya aukaka ararsa zuwa gaban Kaisar, wanda shi ne sarkin Roma, domin ya yanke hukuncin da kansa.—Ayyukan Manzanni 16:37-39; 22:25-28; 25:10-12. ˇ
¯
Ta yaya ake biyan makiyaya a zamanin da?
ALLON DUTSEN DA AKA RUBUTA
KWANGILAR TUMAKI DA KUMA
AWAKI DA AKA SAYA, A WAJEN
SHEKARA TA 2050 K.Z.Y.
Yakubu uban iyali ya yi kiwon garken kawunsa Laban shekara 20.
Yakubu ya fara yi wa Laban aiki na shekara 14 domin ya ba shi
’ya’yansa biyu ya aura, bayan haka, sai ya yi aiki na shekara 6 domin ya sami tumaki. (Farawa 30:25-33) Littafin nan Biblical Ar¯
chaeology Review ya ce: “Marubuta a zamanin da da kuma waanda suka karanta Littafi Mai Tsarki sun san da irin wannan
yarjejeniyar, kamar wanda Yakubu da Laban suka yi.”
¯
Duwatsun da aka rubuta kwangila a zamanin da da aka tono a
birnin Nuzi da Larsa da kuma wasu wurare a asar Irai sun nuna
irin wannan yarjejeniyar. A irin wannan kwangilar, ana rarraba tumaki kowace shekara. Makiyaya suna karan rion tumaki kuma
ana rubuta adadinsu da shekarunsu da kuma jinsinsu. Bayan shekara guda, mai tumakin yana karan ulu da madara da kindirmo da kuma ananan tumaki da dai sauransu. Duk arin da aka
samu na makiyayin ne.
aruwar da aka samu ya dangana ga adadin tunkiyar da aka
ba makiyayin. Ana sa rai cewa tunkiya ari za su haifi ’ya’ya 80.
Makiyayin zai biya idan wani tunkiya ko rago ya ace. Saboda
haka, yana bukata ya kula da dabbar da yake kiwo. ˇ
Yale Babylonian Collection
SATUMBA–OKTOBA 2015
15
AMSOSHIN TAMBAYOYI DAGA LITTAFI MAI TSARKI
Shin yadda rayuwar nan za ta
kasance ke nan?
Ka taa yin tunani cewa ma’anar rayuwa kawai ita ce
yin wasa da aiki da aure da samun yara da kuma tsufa?
(Ayuba 14:1, 2) Littafi Mai Tsarki ya nuna cewa mutane
masu hikima ma sun yi irin wannan tunanin.—Karanta
Mai-Wa’azi 2:11.
Shin rayuwa tana da ma’ana kuwa? Ya kamata mu
fara yin wannan tambayar, Yaya rayuwa ta soma? Yadda Allah ya halicci wawalwarmu da kuma jikinmu ya
sa mutane da yawa sun gaskata cewa akwai Mahalicci
mai hikima. (Karanta Zabura 139:14.) Idan haka ne,
yana da manufa mai kyau na halittar mu. Sanin wannan manufar za ta taimaka mana mu yi rayuwa mai
ma’ana.
KANA GANI MUNA CIKA SAURIN
MUTUWA NE?
Don arin bayani,
ka duba babi na 3
a wannan littafin,
Shaidun Jehobah
ne suka wallafa
Me ya sa aka halicci mutum?
Allah ya albarkaci iyayenmu na farko kuma ya ba su
aiki mai kyau. Manufarsa ita ce su cika duniya da
’ya’ya, su sa ta zama aljanna kuma su rayu har abada a
cikinta.—Karanta Farawa 1:28, 31.
An jinkirta manufar Allah sa’ad da iyayenmu suka
taka dokarsa. Amma Allah bai fid da rai a kanmu ba
kuma bai canja manufarsa ba. Littafi Mai Tsarki ya
gaya mana cewa Allah yana kan aiki tuuru don ya ceci
mutane masu aminci kuma ya aiwatar da manufarsa ga
duniya. Saboda haka, Allah yana so ka ji dain rayuwa
yadda ya nufa tun asali! (Karanta Zabura 37:29.) Yin
nazarin Littafi Mai Tsarki zai sa ka koyi yadda za ka amfana daga nufin Allah.
Za ka kuma iya
samunsa a dandalin
www.jw.org/ha
MENENE Ainihi
LITTAFI MAI
TSARKI YAKE
KOYARWA?
Don Allah ku turo mini littafin nan Menene
Ainihi Littafi Mai Tsarki Yake Koyarwa?
YARE SUNA ADIRESHI Idan kana neman adireshinmu, ka duba shafi na 2
Ka sauko da
wannan mujallar
da na kwanan
baya kyauta
p
Akwai Littafi Mai
Tsarki a harsuna
sama da 100 a
Intane
Ka shiga dandalin
www.jw.org/ha kai
tsaye ko ka yi scan
in wannan alamar
da na’urarka
wp15 09/01-HA
150603
s
n
o
ZA KA SAMI AMSOSHI GA ARIN TAMBAYOYI
GAME DA LITTAFI MAI TSARKI A INTANE